1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Saudiya: Ba mu kai hari a makaranta ba

Abdul-raheem HassanAugust 14, 2016

Saudiya ta ce dakarunta sun kai hari ne a sansanin da mayakan IS ke samun mafaka, amma ta musanta zargin da ake na cewa runduanra sojojin taron dangi da take jagoranta sun kai hari makaranta.

https://p.dw.com/p/1JiC5
Hare-haren Saudiya a Yemen
Hare-haren Saudiya a YemenHoto: DW/M. al-Haidari

Rahotanni dai sun nunar da cewa rundunar taron dangin da Saudiyan ke jagoranta a Yemen da nufin yakar 'yan tawayen Houthi, sun kai hari wata makaranta inda suka hallaka wasu dalibai 10 da jiragen yakinsu yayin wani samame ta sama a garin birnin Haydan da ke lardin Saada. Rundunar hadin kan kawancen sun ce indai ba'a yaba da yunkurin lalata bama bamai a sansonin mayakan da ake zargin kasar Iran na marawa baya ba, bai kamata a zarge su da laifin kai hari da ya hallaka dalibaia a wannan makaranta ba. To sai dai kungiyar likitoci na gari na kowa MSF ta tabbatar da cewa jiragen kawancen yakin ne suka kaddamar da hari a kan makarantar.