1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harin ta´adanci a India ya hallaka mutane 55

February 28, 2006
https://p.dw.com/p/Bv6X

A ƙasar India, wasu mutane ɗauke da makamai sun kai hari a yankin Darmagura, wanda ya hallaka mutane 55, da jikkata wasu kimanin20.

Rahotanin jami´an tsaro, sun ɗora alhakin wannan hari, ga yan tawaye, wanda shine mafi muni a tsawan shekaru 30 da su ka wuce a ƙasar.

Yan tawayen sun kai harin, da nufin rugurguza wani sansani na mutanen da ke bada goyan baya ga gwamnati.

A halin yanzu, an baza jami´an tsaro da dama domin farautar yan tawayen.

Harin ya wakana, a jajibirin ziyara da shugaban Amurika Georges Bush, zai kai a kasar India.