Harkokin siyasa a Zambia sun fara kan kama
March 1, 2006Jam´iyyun adawa uku na kasar Zambia sun cimma yarjejeniyar fitar da dan takara daya da zai kalubalanci shugaba Levy Mwanawasa a zaben shugaban kasa da ake shirin gudanarwa.
A cewar mai magana da yawun jam´iyyun hadin gwiwar na UDA, jam´iyyar tasu zata gudanar da babban taro a nan gaba kadan don zaben mutumin da zai musu wannan takara.
Daukar wannan mataki dai a cewar kakakin jam´iyyar ta UDA, yazo ne a bisa muradin yan kasar na fitar da mutumin dai zai fafata da shugaba mai ci a neman wannan mukami.
Masu nazarin siyasa dai na kallon wannan mataki a matsayin wata kafa da shugaba Mwanasawa zai fuskanci babban kalubale a kokarin da yake na yin tazarce a gadon mulkin kasar a karo na biyu.
Rahotanni dai sun tabbatar da cewa babu wata tsayayyiyar rana ta gudanar da wannan zabe, to amma bayanai sun nunar da cewa watakila ya kasance a karshen wannan shekara da muke ciki.