1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Harkokin siyasar kasar Masar

Mohammad Nasiru AwalFebruary 10, 2005

Har yanzu gwamnatin shugaba Hosni Mubarak ba ta aiwatar da sahihan canje-canjen demukiradiya a cikin kasar Masar

https://p.dw.com/p/BvdG
Shugaba Hosni Mubarak na Masar
Shugaba Hosni Mubarak na MasarHoto: AP

A farkon wannan shekara daukacin ´yan kasar Masar sun yi fatan ganin sauye-sauyen siyasa da yawa a cikin kasar, musamman bayan rantsad da sabuwar gwamnati karkashin FM Ahmed Nazif a lokacin bazara na bara. Shi dai Nazif matashi ne sabon jini wanda ya yi karatun jami´a a kasar Kanada. Hakazalika majalisar ministocinsa ta kunshi hanshakan ´yan kasuwa masu neman sauyi.

A cikin watan oktoban bara ne kuma hukuma ta amince da kafuwar wata sabuwar jam´iya mai suna El-Ghad, wadda ta kasance mai sassaucin ra´ayi kuma amintacciya ga matasa. Shi yasa ba abin mamaki ba ne da a cikin lokaci kankane jam´iyar ta samu dubban magoya baya. A cikin wannan watan ne kuma daruruwan masu ilimi da kuma ´yan adawan kasar suka amince da wani kuduri wanda a ciki suka nuna bukatar bawa jama´a damar zaben shugaban kasa tare da kayyade wa´adin shugabancinsa.

Sannan a karon farko hukumomin kasar sun bawa ´yan adawa da shugaba Hosni Mubarak wanda ya shafe shekaru 25 akan karagar mulki, izinin yin zanga-zangar kin lamirin gwamnati. A farkon watan janerun wannan shekara kuma ´yan takarar shugaban kasa da dama sun yi rajista a kuri´ar raba gardama da ake shirin yi a karshen shekara. Sannan a cikin wani jawabi da yayi a ranar 9 ga watan janeru shugaba Mubarak yayi lale marhabin da ´yan takarar da suka nuna sha´awar shiga cikin wannan zabe.

To amma wai shin ko hakan na nufin kenan iskar canji ta fara kadawa a fagen siyasar kasar ta Masar kamar yadda wasu suka dade suna bege? Ba a kuwa dade ba sai murna ta koma ciki musamman ga ´yan adawa. Domin a jajibiren zaben Iraqi lokacin da shugaba Mubarak ke kan hanyar zuwa Nijeriya don halartar taron kolin kungiyar tarayyar Afirka, ya sanar da cewar ba zai yarda a gudanar da wata kuri´ar raba gardama da zata ba da damar yin zaben shugaban kasa ba, domin tsarin da kasar ke bi yanzu shine mafi a´ala kuma mafi dacewa wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a cikin kasar ta Masar.

A ma halin da ake ciki hukumomin kasar na ci-gaba da tsare ´yan adawa, musamman shugabannin sabuwar jam´iyar nan ta Al-Ghad. Wasu masharhanta dai na da ra´ayin cewa ba za´a samu wani canji a tsarin mulki irin na kama karya a Masar ba. Hasali ma daukacin al´umar kasar sun fi damuwa ne akan neman abin sakawa bakin sallati maimakon mayar da hankali akan al´amuran siyasa. Bugu da kari dukkan jam´iyun kasar ciki har da ta gwamnati da kuma na ´yan adawa ba su da fari jini. Hatta jam´iyar ´yan´uwa musulmi ta Muslim Brotherhood wadda ta yi tashe a cikin shekarun 1990, yanzu haka talakwan kasar sun juya mata baya.

Wani abin da ake fargaba yanzu haka dai shine shugaba Mubarak mai shekaru 76 a duniya ka iya nada dansa wato Jamal wanda masani ne a harkar zuba jari na bankuna, a matsayin wanda zai gajeshi a mukamin shugaban kasa.