1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumar leken asirin Jamus ta musanta ba dakarun Amirka taimako

January 13, 2006
https://p.dw.com/p/BvCX

Tsohuwar gwamnatin SPD da kuma The Greens ta yi kanekane a rikicin Iraqi fiye da yadda aka sani kawo yanzu. Ministan harkokin wajen Jamus Frank-Walter Steinmeier da kuma hukumar leken asirin Jamus ta BND sun tabbatar da cewa an tura ma´aikatan hukumar zuwa birnin Bagadaza a lokacin yakin Iraqi. To amma sun musanta rahotannin cewar jami´an sun taimakawa sojojin Amirka a Iraqi. Da farko dai kafofin yada labarun Jamus da dama sun rawaito cewar a cikin shekara ta 2003, jami´an hukumar ta BND sun taka rawa a wani hari da sojojin kawance suka kai kan wani gidan cin abinci dake Bagadaza, inda aka halaka akalla fararen hula 12. Yanzu haka dai jam´iyun adawa sun yi kira da a gudanar da bincike akan rawar da hukumar ta taka a yakin Iraqi da kuma yakin da Amirka ke yi da ta´addanci na kasa da kasa.