1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumar Tarayyar Turai ta ja hankalin Macron

May 8, 2017

Shugaban hukumar Tarayyar Turai Jean-Claude Juncker ya yi kiran shugaban kasar Faransa mai jiran gado da ya tabbatar da daukar matakan rage barnata kudin gwamnati da zarar ya kama madafu.

https://p.dw.com/p/2cdG9
Italy EU Florenz Jean-Claude Juncker
Hoto: picture-alliance/AP Photo/M. degl'Innocenti

A cewar Mr. Jean Claude Juncker ba kananan kudade ne ake barnatarwa ga banza ba a Faransa a yanzu.

A nata bangaren gwamnatin Jamus kuwa cewa ta yi za ta taimakawa Mr. Macron ta fuskar samarwa faransawa ayyuka.

Emmanuel Macron, shugaban Faransar na 25 ya sami nasara gagaruma a babban zaben kasar na karshen mako inda Jamus ke alkawarin hada kai da shi wajen tabbatar da daidaito a nahiyar Turai.

A cewar shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel dangantakar manyan kasashen na Turai, babban ginshiki ne a tsarin alakar Jamus da kasashen ketare musamman kan batutuwan da suka shafi hulda ta amana tsakaninsu.