1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Hukumomin leken asirin Syria da Lebanon na da masaniya akan kisan Hariri

October 21, 2005
https://p.dw.com/p/BvOU

Wani binciken da MDD ta yi ya nuna cewa manyan jami´an leken asirin kasashen Syria da Lebanon na da hannu a kisan gillan da aka yiwa tsohon FM Lebanon Rafik Hariri. Kamar yadda rahoton wanda mai shari´a Detlev Mehlis na nan Jamus ya nunar, kisan na Hariri a ranar 14 ga watan fabrairu na da daure kai ta yadda da wuya a iya gane cewar hukumomin leken asirin Syria da Lebanon ba su da wata masaniya dangane da kisan. Rahoton mai shafuka 53 ya bayana cewar har yanzu ba´a kammala binciken ba kuma dole za´a ci-gaba da wannan bincike tare da hadin kan hukumomin shari´a da na tsaron Lebanon. A jiya an girke sojoji da ´yan sanda kimanin dubu 10 a fadin kasar ta Lebanon a wani mataki da jami´ai suka bayyana da cewa dokar ta baci a fakaice.