1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran da Saudiyya sun tattauna kan Hajji

March 5, 2017

A wani matakin sulhu gabanin aikin hajjin bana Iran da Saudiyya sun tattauna domin warware sabanin da ke tsakaninsu bayan tsamin danganta da ta kai ga Saudiyya ta haramta wa 'yan kasar Iran zuwa aikin hajjin.

https://p.dw.com/p/2Yfdl
Mekka Saudi Arabien - Muslime bei Kaaba
Hoto: picture-alliance/AA/O. Akkanat

Iran ta ce an sami ci gaba mai ma'ana a tattaunawa da kasar Saudiyya domin barin 'yan kasar su gudanar da aikin hajjin bana duk da cewa akwai sauran batutuwa da ba'a kammala cimma matsaya a kansu ba.

A shekarar bara ce dai Saudiyya ta haramta wa 'yan Iran shiga kasar domin aikin hajji bayan da dangantakar diplomasiyya ta lalace tsakanin kasashen biyu da suka kuma suka kasa cimma daidaito kan matakan tsaro a lokacin aikin hajjin.

Kamfanin dillancin labaran Iran ya ruwaito wakilin jagoran addini na kasar Ali Ghazi yana cewa an warware galibin matsalolin da ke tsakanin kasashen, sai wasu 'yan kananan batutuwa kawai da suka rage.