1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran ta yi tir da kalaman shugaba Chirac na Faransa

January 22, 2006
https://p.dw.com/p/BvB6

Iran ta yi Allah wadai da sanarwar da shugaban Faransa Jacques Chirac ya bayar a tsakiyar makon jiya cewar Faransa na da ´yancin yin amfani da makaman nukiliya a kan kasar da ta kaddamar da ta´addanci a kanta. Wata sanarwa da ma´aikatar harkokin wajen Iran ta bayar ta ce barazanar ta shugaba Chirac ta fito da aniyar kasashen duniya masu mallakar makan nukiliya a fili. Shi ma shugaban bangaren jam´iyar SPD a majalisar dokokin Jamus Peter Struck ya nesanta kanshi daga kalaman na shugaba Chirac. Struck ya ce ba ya tsammanin za´a iya yakar ayyukan ta´addanci da wani harin makamin nukiliya. Gwamnatin Jamus dai ba ta fito karara ta yi Allah wadai da furucin na shugaba Chirac ba. A kuma halin da ake ciki Isra´ila ta sake gargadin Iran game da shirinta na kera makaman nukiliya. Ministan tsaro Shaul Mofaz ya yi tir da kalaman shugaba Mahmud Ahmedi-Nijad na yin kira da a goge Isra´ila daga taswirar duniya.