1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Al'ummar Iran na zaben 'yan majalisar dokoki

Yusuf BalaFebruary 26, 2016

Zaben da ke zama na farko tun bayan da kasar ta warware rikicinta da kasashen duniya kan batun shirinta na makamin nukiliya.

https://p.dw.com/p/1I2e0
Iran Teheran Die Wahlen zum Parlament und Expertenrat Ali Khamenei
Ali Khamenei ke kada kuri'arsa a zaben IranHoto: khamenei.ir

Al'ummar kasar Iran sun fita tashoshin kada kuri'a dan zaben mambobi na majalisar dokokin kasar 290 da ma majalisar kwararrun malamai mai mambobi 88 wadanda ke zabe ko ma su saukar da shugaban addini da ke zama kololuwa a kasar, tuni shugaban addini na kasar Ayatollah Khamenei ya kada kuri'arsa a wannan zabe.

Zaben da ke zama na farko tun bayan da kasar ta warware rikicinta da kasashen duniya kan batun shirinta na makamin nukiliya.

An dai bude tashoshin kada kuri'a 53,000 a fadin kasar yayin da mutane miliyan 55 'yan kasar ta Iran ke zama wadanda suka cancanci kada kuri'a.