1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Iran zata gina sabbin tashoshin makamashin nukiliya

April 22, 2006
https://p.dw.com/p/Bv15
Jakadan Iran a hukumar MDD mai sa ido a ayyukan nukiliya ta kasa da kasa, IAEA ya ce kasar sa ta kulla wani shirin hadin guiwa don samar da sinadarin uranium a cikin Rasha. To amma har yanzu ana nazari kan ka´idojin yarjejeniyar. Ali Asghar Sultani bai yi bayani ba ko shirin hadin guiwar sarrafa uranium din zai maye gurbin tace wannan sinadari da ake yi a cikin kasar ta Iran. Har yanzu dai hukumomin kasar sun dage cewa zasu bijirewa kiran da MDD ta yi kana kuma zasu ci-gaba da tace sinadarin uraniuma cikin kasar. Tun a cikin watan fabrairu ma Iran ta taba ba da sanarwar cimma irin wannan yarjejeniya da Rasha, amma ba´a samu wani ci-gaba ba saboda kin da gwamnatin Teheran ta yi na dakatar da shirin bunkasa uranium a cikin gida. A wani labarin kuma gwamnatin Islama ta Iran ta ce a cikin wata mai zuwa zata gaiyaci kamfanoni daga ko-ina cikin duniya don neman kwangilar gina wasu sabbin tashoshin samar da makamashin nukiliya guda biyu a cikin kasar.