Iran,babu gudu babu ja da baya
March 30, 2006Talla
Jakadan kasar Iran a hukumar kula da yaduwar nuclear ta mdd ya bayyana cewa ,tehran bazata dakatar da sarrafa sinadran uranium ba, wanda zai iya samar da makamashi ,tare da kera boma bomai a hannu guda ,kamar yadda komitin sulhun mdd ta bukaceta datayi.A jiya nedai wakilan komitin sulhun baki dayansu suka amince da kira ga Iran data dakatar da harkokinta na Uranium.To sai dai a hiran da yayi da manema labaru ta wayan tangaraho jakadan tehran din dake hukumar ta IAEA ,Aliasghar Soltaniyeh,yace ba zasu dakatar da sarrafa sinadran uranium dinsu ba,domin suna yine da nufin samar da makamashi wa alummar kasar,amma ba da nufin kera makamai kamar yadda