1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

IS ta kashe mayakan sa-kai a Iraki

February 19, 2018

Kungiyar IS ta halaka wasu mayakan sa-kai 'yan Shi'a su 27 wadanda ke aiki da sojojin kasar Iraki, a yankin kudu maso yammacin birnin Kirkuk.

https://p.dw.com/p/2svUn
Syrien FSA Kämpfer Angriff auf Afrin
Hoto: Getty Images/AFP/N. Al-Khatib

Mayakan kungiyar IS a kasar Iraki, sun halaka wasu mayakan sa-kai 'yan Shi'a su 27 wadanda ke aiki da sojojin kasar, a yankin kudu maso yammacin birnin Kirkuk. Lamarin dai ya faru ne yayin da mayakan na IS suka yi wa 'yan Shi'an kwantan bauna lokacin wani sintirin dare, kamar yadda majiyar mayakan na sa kai ta tabbatar.

Maharan na IS sun yi badda sawu ne cikin kayan soji, inda suka afka masu, suka kuma yi musayar wuta na akalla sa'o'i biyu. Wasu bayanai ma dai sun tabbatar da mutuwar wasu daga cikin mayakan na tarzoma.