1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jacob Zuma na shirin fuskantar shari'a

Abdourahamane HassaneApril 29, 2016

Yau aka shirya wata kotu a Afirka ta Kudu za ta bayyana hukuncin a kan ko za ta mayar da tuhume-tuhumen da ake yi wa Shugaba Jacob Zuma da aikata laifuka na cin hanci guda 700 ko akasin haka.

https://p.dw.com/p/1If32
Südafrika Kapstadt Jacob Zuma Präsident Anhörung Parlament
Hoto: picture-alliance/dpa/N. Bothma

An dai samu Jakob Zuma a shekara ta 2007 da laifin cin hanci,da rashin biyan kuɗaɗen haraji da kuma cinikin makamai na kusan dala biliyan huɗu da rabi tun a lokacin yana shugaban jam'iyyar ANC.Amma a shekara ta 2009 kotun ta janye tuhumar makonnin kadan kafin a zaɓeshi a matsayin shugaban ƙasa.

Saboda a lokacinh lauyoyin Jacob Zuman sun riƙa satar sauraon wayoyin salula tsakanin babban alkalin kotun da kuma wani babban jami'in 'yan sanda na ƙasar,
domin shawo kan kotun don nuna ma ta cewar makirci ne kawai aka shirya wa Zuma abin da ya sa kotu ta yi watsi da tuhume-tuhumen.