1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jagorar jam'iyyar AfD ba ta da niyyar shiga zabe

Yusuf Bala Nayaya
April 19, 2017

A karshen mako ne dai jam'iyyar mai adawa da baki za ta yi babban taro inda anan ne za ta zayyana 'yan takara da za su jagoranci jam'iyyar ta AfD a kokari na danganawa majalisar dokokin Jamus.

https://p.dw.com/p/2bVuA
Deutschland Frauke Petry, AfD
Hoto: Getty Images/AFP/J. MacDougall

Frauke Petry, jagorar jam'iyyar masu adawa da baki ta AfD  ta bayyana a ranar Laraban nan cewa ba za ta jagoranci yakin neman zaben jam'iyyar ba a zaben ranar 24 ga watan Satimba.

A jawabin da ta fitar na bidiyo a shafinta na Facebook ta yi jawabi kamar haka:

"A kokari na kawo karshen duk wani cece-ku-ce  na yi wannan hoton bidiyo inda na ke cewa babu wani tsari daga bangarena na jagorantar jam'iyyar a matsayin 'yar takara ko shiga a dama da ni a neman wata babbar kujerar shugabanci".

A karshen mako ne dai jam'iyyar za ta yi babban taro inda anan ne za ta zayyana 'yan takara da za su jagoranci jam'iyyar ta AfD a kokari na danganawa majalisar dokokin Jamus a karon farko.