1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jam'iyyar AfD ta kayar da CDU ta Merkel

Abdullahi Tanko/AHSeptember 4, 2016

Sakamakon farko na zaben 'yan majalisar dokoki a jihar Mecklenburg-Vorpommern ta Jamus na nuna cewar jam'iyyar CDU ta shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta sha kaye a hannun jam'iyyar da ke kyamar da baki wato AfD.

https://p.dw.com/p/1Jvep
Deutschland Landtagswahl Mecklenburg-Vorpommern AfD
Hoto: Reuters/H. Hanschke

A bisa alkaluman kididdiga da gidan Talabijin na ZDF ya fitar, Jam'iyyar Afd mai kyamar baki ta sami kashi 21.5 cikin dari na kuri'un da aka kada.Hakan na nufin cewar a karon farko jam'iyyar za ta shiga majalisar dokokin jihar ta arewa maso gabashin Jamus. Da ma dai tana da wakilai a majalisun dokoki a jihohi takwas na tarayyar Jamus.Akwai kuma yiwuwar cewar jam'iyyar na iya samun damar shiga majalisar tarayya ta kasa a babban zabe da za'a yi a shekara mai zuwa.

A waje guda dai Jam'iyyar CDU ta shugabar gwamnati Angela Merkel ta sami kashi 20 ne cikin dari na kuri'un da aka kada a zaben na yau, wanda ke nufin cewar ta fado zuwa matsayi na uku a jerin jam'iyyun da ke da karfi a jihar ta Mecklenburg Vorpommern . Mutane kimanin miliyan daya da dubu dari uku ne suka kada kuri'a zaben.