1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jam'iyyar SPD ta lashe zabe a Berlin

Abdul-raheem HassanSeptember 19, 2016

Jami'iyyar CDU ta shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta kuma sha kaye a zabubbukan 'yan majalisu da ya gudana a birnin Berlin .

https://p.dw.com/p/1K4g4
Deutschland Berlin Wahl SPD
Hoto: picture-alliance/Pacific Press/S. Kuhlmey

A yanzu dai ta tabbata cewa Jam'iyyar SPD ce za ta kasasnce jam'iyya mafi karfi da ikon fada a aji a majalisar jihar, biyo bayan lashe zaben 'yan majalisun jihohi da jam'iyyar ta yi a zaben da ya gudana a karshen mako inda jam'iyyar ta SPD ta samu kashi 21.6 a zaben, yayin da Jam'iyar CDU ta shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ke da kashi 18 cikin dari na kuri'un da aka kada, kana jami'yyar AFD ta masu kyamar baki a kasar da kashi 14.2 cikin dari.

Sakamakon zabubukan da ya nuna jam'iyyar CDU a matsayin ta biyu, na bayyana cewar jam'iyyar za ta rasa mulki a kawancen babban birnin kasar Jamus. To sai dai masu nazarin al'amuran siyasa dai na danganta rashin nasara da jam'iyyar CDU ta shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ke fuskanta a zabubbun kasar, baya rasa nasaba da yadda ta rungumi manufofinta a kan 'yan gudun hijira.