1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jammeh ya zargi ECOWAS da takalar yaki

Yusuf Bala Nayaya
January 1, 2017

A sakonsa na sabuwar shekara, shugaban Gambiya Yahya Jammeh ya ce matsayar da kungiyar ECOWAS ta cimma ya sabawa dokarta na kaucewa tsoma baki a harkokin cikin gidan wata kasa.

https://p.dw.com/p/2V7Q9
Gambia Wahlen Yahya Jammeh
Hoto: picture alliance/AP Photo/J. Delay

Shugaba Yahya Jammeh ya zargi ECOWAS da aiyana yaki a kasarsa bayan da ta nemi ya sauka daga mulkin kasar sakamakon shan kayi da ya yi a zaben kasar. Kungiyar dai ta ECOWAS da ke da wakilci daga kasashe 15 na Yammacin Afirka ta bayyana cewa sakamakon zabe da aka yi a ranar daya ga watan Disambar bara ya halasta.

Shugaba Jammeh dai a sakonsa na sabuwar shekara a daren ranar Asabar ya ce matsayar da Kungiyar ECOWAS ta cimma ya saba wa dokarta na kaucewa tsoma baki a harkokin cikin gidan wata kasa. A cewarsa abin da kungiyar ta bayyana tamkar aiyana yaki ne a kasarsa da ma yi wa kasar kutse a kundin tsarin mulkinta, kuma abu ne da ba zai lamunta ba. Shugaban ya ce kasar ba za ta daga kafa ga kowa ba, kuma a shirye ta ke ta yaki duk wanda ya takaleta.

Zaben kasar ta Gambiya dai na watan Disambar bara ya bayyana madugun 'yan adawar kasar Adama Barrow a matsayin wanda ya lashe shi, sakamakon tda Shugaba Jammeh da ya shafe shekaru 22 a karagar mulki ya amince da shi  kafin daga bisani ya sauya matsayi.