1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus: CDU ta lashe zabe a jihar Saarland

Lateefa Mustapha Ja'afar
March 26, 2017

Jam'iyar Christian Democrats (CDU) ta shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta samu nasara a zaben da aka gudanar a jihar Saarland da ke yankin Kudu maso Yammacin kasar.

https://p.dw.com/p/2ZzSw
Magoya bayan jam'iyyar CDU a Jamus na murnar lashe zabe a jihar Saarland
Magoya bayan jam'iyyar CDU a Jamus na murnar lashe zabe a jihar Saarland Hoto: picture-alliance/dpa/O. Dietze

Rahotanni sun nunar da cewa jam'iyyar ta CDU nada sama da kaso 40 cikin 100 na kuri'un da aka kada yayin da abokiyar hamayyarta ta Social Democrat (SPD) ke da sama da kaso 30 cikin 100 na kuri'un. Wannan dai na nuni da cewa akwai sauran aiki gagarumi a gaban jam'iyyar ta SPD, a fatan da take da shi na lashe zaben shugabancin gwamnati a Jamus din, bayan da ta tsayar da Martin Schulz a matsayin dan takararta da zai kalubalanci Merkel a zaben da za a gudanar a watan Satumba mai zuwa a kasar.