1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus ta karrama Desmond Tutu

Ibrahim SaniDecember 3, 2007
https://p.dw.com/p/CVvx

Jamus ta karrama shugaban addinin kirista na ƙasar Afrika ta kudu, wato Desmond Tutu da lambar yabo mafi girma ta ƙasar. Tsohon Archbishop ɗin ya samu lambar ne, a sakamakon ayyukansa na wa´azin wanzar da zaman lafiya. Ƙaramar minista a ma´aikatar tattali da raya ƙasashe ta Jamus, Hedemarie Wieczorek-zeul ta ce lambar yabon na a matsayin alamace ta zaman lafiya da adalci a Duniya. Ministar ta kuma tabbatar da cewa Desmond Tutu, mutunne daya fita zakka a tsakanin tsaransa, dangane da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Afrika ta kudu. Desmond Tutu mai shekara 76, ya taɓa karɓar kyautar Nobel ta zaman lafiya a shekara ta 1984.