1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus za ta aika sojojin1,200 don yakar IS

Kamaluddeen SaniDecember 1, 2015

A wannan Talatar nan ce majalisar zartawar gwamnatin Jamus ta amince da tura dakarun a kawancen da kasashe suke na hada rundunar da za ta yaki kungiyar IS da ke a Siriya.

https://p.dw.com/p/1HFYg
Afghanistan Deutschland Bundeskanzlerin Merkel zu Kurzbesuch in Masar-i-Sharif
Hoto: dapd

Majalisar ministocin ta dauki matsayin ne domin tallafawa Faransa da kuma kasashen da ayyukan kungiyar IS ya shafa, a inda tallafin ya hada da jiragen yaki da kudade.

A cewar ministan harkokin wajen Jamus Frank-Walter Steinmeier, suna yin duk abinda ya wajaba ne, ta fuskar matakan soji domin tinkarar ayyukan kungiyoyin ta'adda.

Amincewar dai na yin nuni da cewar Jamus ta amsa kiran Faransa kan tallafin da take nema, don dakile ayyukan kungiyar IS da ta kai hare-hare a birin Paris kwanakin baya.