Jamus zata taimakawa wajen gina kasar Iraqi
January 11, 2006Talla
Mahukuntan Jamus sun sanar da matakin taimakawa Amurka a kokarin da take na kara gina kasar Iraqi bayan yaki.
A cewar kakakin gwamnatin kasar, wato Thomas Steg, mahukuntan na Jamus na shirin fadada horon da dakarun sojin kasar ke bawa jami´an yan sandan kasar ta iraqi.
Bugu da kari, akwai kuma shirin kara yawan kudaden tallafi ga Mdd don ci gaba da bawa matasa horo na koyon sana´oi a kasar ta Iraqi.
Ana sa dai ran tabbatar da wannan shiri daga bakin shugabar gwamnati Angela Merkel a lokacin ganawar su ta keke da keke da shugaba Bush da ake sa ran yi a jibi Juma´a.