1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamusawa 5 sun rasa rayukan su a Pakistan

October 5, 2010

Jimlar mutun 8 ne suka rasa rayukkan su a hare-haren da hukumar CIA ta kai a Pakistan

https://p.dw.com/p/PVvZ
Hoto: picture-alliance/dpa

Aƙalla Jamusawa 5 suka rasa rayukan su, sakamakon wani harin da aka ƙaddamar a yankin arewa maso yamacin Pakistan. Jami'an leƙen asiri na cikin gida a kasar Pakistan, sun ce kimanin mutane 8 ne suka rasu, a wani hari da hukumar leƙen asirin Amurka ta CIA ta kai a yankin, da jiragen sama masu sarrafa kansu da kansu. 5 daga cikin su Jamusawa ne 'yan asalin kasar Turkiyya. A yayin da aka kai harin, makaman rokoki biyu ne suka lalata wani gida da ke garin Mirali a arewacin Waziristan inda ke da iyaka da ƙasar Pakistan. Yankin na Waziristan ya yi kaurin suna wajen zama maɓoyar 'yan tawayen da ke da alaƙa da ƙungiyoyin Taliban da na Alƙaida.

Mawallafiya: Pinado Abdu

Edita: Umaru Aliyu