1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jiran sakamakon zaben shugaban kasa a Burkina Faso

November 14, 2005
https://p.dw.com/p/BvL9

A kasar Burkina Faso an kammala zaben shugabn kasa lami lahia.

A halin da ake ciki a na shiga jiran sakamako.

Saidai hukumar zabe mai kanta ta sanar cewa duk da fara kidayar kuri´u da a ka yi ba za a samu sakamakon ba sai nan da kwanaki 3 masu zuwa.

Tunni sarkin yakin zaben jam`iyar CDP ta shuga Blaize Kompaore ya shaidawa manema labarai cewa dan takara su za shi lashe zaben tun zagaye na farko, da kashi 65 zuwa 70 na yawan kuri`un da a ka jefa.

Wakilan kungiyar tarayya Afrika sun yabawa zaben tare da bugun gaban cewa wata shaide ce mai nuna Demokradiya ta nuna a kasar Burkina Faso.

Sun kuma tabatar da an gudanar da zaben cikin adalci da ta kamata.