1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kalubale ga Angela Merkel a taron CDU

Lateefa Mustapha Ja'afarDecember 14, 2015

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel na ci gaba da fuskantar suka dangane da matakin yin maraba da 'yan gudun hijira da ta dauka.

https://p.dw.com/p/1HMos
Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel
Hoto: picture-alliance/dpa/M. Kappeler

'Yan sa'oi kalilan gabanin babban taron kasa na jam'iyyarta ta CDU a Karlsruhe, ta sake fuskantar suka daga 'ya'yan jam'iyyar tata da ke cewa ya kamata a takaita yawan 'yan gudun hijirar da Jamus din ke karba. Sun dai fitar da wata sanarwa da ke dauke da bayanai na cewa yawan 'yan gudun hijirar da ke shigowa Jamus ka iya sanya kasar cikin halin tsaka mai wuya. Merkel dai ta dade ta na fuskantar suka daga bangarori da dama ciki kuwa har da jam'iyyar tata ta CDU dangane da batun 'yan gudun hijirar.