1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kalubalen da ke a gaban Angela Merkel

Abdourahamane Hassane
September 28, 2017

Bayan kammala zaben Jamus wanda Jam'iyyar CDU ta Angela Merkel ta samu nasara, yanzu haka hankali ya karkata dangane da tattaunawar da shugabar gwamnatin za ta yi da sauran jam'iyyun siyasar don kafa gwamnati.

https://p.dw.com/p/2kryp
Berlin Jamaika-Koalition
Hoto: picture-alliance/dpa/P. Endig

Za a dai kwashe kwanaki shugabar gwamnatin ta Jamus Angela Merkel tana tattaunawa da jam'iyyun siyasar, misali FDP da kuma ja'imyyar masu fafutukar kare muhali watau Grüne wajen kafa gwamnati. Sai dai kuma akwai sabani tsakanin jam'iyyun a game da batun bakin haure da na kungiyar EU, abin da ake gani zai kasance mai wahala ga shugabar gwamnatin wajen samun abokanan tafiya.