1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kalubalen ilimin mata 'yan gudun hijira a duniya

Salissou Boukari MNA
March 7, 2018

Wani rahoton Majalisar Dinkin Duniya ya nunar cewa, yara 'yan mata sun fi fuskantar tarin matsalolin da ke hana su samun damar yin karatu har ya zuwa makarantun sakandare kamar 'yan uwansu maza a duniya.

https://p.dw.com/p/2trqr
Zentralafrikanische Republik Schüler
Hoto: imago/CHROMORANGE

Rahoton da aka fitar a jajibirin ranar mata na duniya, ya ce wannan matsala ta fi kamari ne a tsakanin 'yan gudun hijira da suka bar gidajensu sakamakon rikice-rikice a sassan duniya, kamar yadda babban jagoran hukumar kula da 'yan gudun hijira na Majalisar Dinkin Duniya ta HCR, Filippo Grandi ya sanar.

Rahoton ya ce rabin yara 'yan gudun hijira miliyan 3.5 da ke a fadin duniya, ba su samun zuwa makaranta ba, wanda kuma matsalar an fi samunta ne a makarantun sakandare zuwa na gaba da sakandare kamar yadda rahoton na HCR ya sanar, inda ya ce a cikin kasashe irin su Kenya, da Habasha, lamarin ya fi kamari.