1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kamaru: Kotu ta wanke Ahmed Abba na RFI

Gazali Abdou Tasawa
December 21, 2017

Kotun sojojin Kamaru ta wanke a Ahmed Abba dan jaridar nan wakilin sashen Hausa na gidan rediyon Faransa na RFI a kasar, daga babban zargin da ake yi masa na halasta kudaden haram da kuma gudanar da ayyukan ta'addanci. 

https://p.dw.com/p/2pn7T
Karte Kamerun Mamfe Bamenda Buea DEU

Kotin ta bayyana wannan hukunci ne a zaman da ta yi kan daukaka karan da dan jaridar ya yi a gabanta kan hukuncin farko na zaman wakafi na shekaru 10 da tarar kudin Euro dubu 85 da ta yanke masa a shekara ta 2016. Sai dai kuma bayan da ta wanke shi daga laifin farko kotun ta yanke masa hukuncin zaman kaso na watanni 24 a bisa samunsa da laifin boye asirin ayyyukan ta'addancin da ya ke da masaniya a kansu. A watan Yulin 2015 ne dai mahukuntan kasar ta Kamaru suka kama dan jaridar a birnin Maroua na arewacin kasar inda ya je aiko da rahotanni kan rikicin Boko Haram.