1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kamitin Sulhu ya gaza cim ma daidaito kan batun Iran.

May 10, 2006
https://p.dw.com/p/Buyy

Ministocin harkokin waje na ƙasashe masu kujerun dindindin a kwamitin sulhu na Majalisar Ɗinkin Duniya da na Jamus, sun gaza cim ma madafa kan batun zartad da ƙuduri game da rikicin da ake yi kan shhirye-shiryen makamashin nukiliyan Iran. Yayin da Birtaniya da Faransa da Amirka ke fafutukar neman a sanya wa Iran ɗin takunkumi ko ma ɗaukan soji a kanta, idan ba ta dakatad da ayyukan inganta yureniyum da take yi ba, ƙasashen Sin da Rasha na adawa da wannan yunƙurin.

Ministan harkokin wajen Jamus, Frank-Walter Steinmeier, wanda shhi ma ke halartar taron ministocin a birnin New York, ya ce har ila yau da akwai wasu maganganu guda 6 da ba a warware su ba tukuna, kuma za a bukaci har tsawon mako biyu kafin a iya cim ma yarjejeniya.