1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasar Eritiriya ta yi tir da harin Habasha

Abdul-raheem HassanJune 13, 2016

Dakarun kasar Habsha sun kutsa kai iyakar kasarsu da Eritiriya bayan da suka kaddamar da hari akan iyakokin kasashen biyu, lamarin da ya tayar da jijiyoyin wuya.

https://p.dw.com/p/1J5n0
Bildergalerie Somalia Sicherheitslage Baido 2012
Hoto: JENNY VAUGHAN/AFP/Getty Images

Gwamnatin Kasar Eritiriya ta soki lamarin makwabciyarta Habasha kan kaddamar da hari a kan iyakarta. Mazauna yankin da ke kan iyakar kasashen biyu sun shaida wa kamfanin dillancin labaru na Reuters cewar sun ta jin harbe-harben bindigogi tun a ranar Lahadi har zuwa Litinin. Wasu shaidu sun kuma bayyana cewar sun ga dakarun kasar Habasha na kutsa kai i zuwa yankin na Eritiriya.

Kawo yanzu dai, babu wani martani daga bangaren gwamnatin kasar ta Habasha a kan wannan takaddamar, to sai dai daman akwai takun saka tsakanin kasashen biyu da ke makwabtaka da juna wanda yayi sanadiyar salwantar rayuka da dama a shekarun 1998 i zuwa 2000.