1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasar Gini ta kawar da cutar Ebola

Gazali Abdou TasawaDecember 29, 2015

Hukumar lafiya ta Duniya WHO ta sanar da kawo karshen annobar cutar Ebola a kasar Guinea makonnin shida bayan warkar da mutun na karshe da ya kamu da cutar

https://p.dw.com/p/1HUsR
Liberia Ebola EINSCHRÄNKUNG
Hoto: Brot für die Welt/Christoph Püschner

A wannan Talata ce Hukumar lafiya ta Duniya wato WHO ko OMS ta bayyana a hakumance kawo karshen annobar cutar Ebola kwata-kwata daga kasar Guinea makonnin shida bayan warakar mutun na karshe da ya kamu da cutar a kasar.

Kasar Guinea ta kwashe shekaru biyu tana fama da annobar cutar ta Ebola wace ta halaka mutane dubu biyu da 536 daga cikin dubu uku da 804 da suka kamu da cutar.

Tun a ranar 16 ga wannan wata na Nowamba ne dai aka bayyana warakar Noubia wata jaririya da mahaifiyarta ta haifata da cutar a cibiyar kula da masu dauke da cutar Ebola ta birnin Konakry.