1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasar Sin ta gargadi Mdd kan kasar Burma

October 9, 2007
https://p.dw.com/p/Bu8n

Kasar sin tace yakamata ayi taka tsantsan wajen sakawa kasar Burma takunkumi.Wannan gargadin dai yazo ne a yayin da wasu kasashe ke kiran Mdd data dauki tsauraran matakai a kann kasar ta Burma. Kasar ta Sin, wacce kawa ce ga kasar ta Burma a harkokin kasuwanci, ta kara da cewa akwai bukatar kwamitin sulhu yin karatun mun natsu, don daukar matakin daya dace akan kasar ta Burma. A dai cikin makon nan ne kwamitin sulhu na Mdd da kungiyyar Eu zasu tattauna matakin daya kamata a dauka akan kasar ta Burma. Kasar ta Sin dai na daya daga cikin mambobi na kwamitin sulhun na Mdd, wanda hakan ya bata damar hawa kujerar naki ga duk al´amarin da bai mata dadi ba.