1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasar sin ta yunkura wajen dakile cutar murar tsuntsaye

February 9, 2006
https://p.dw.com/p/Bv8j

Jami´an kiwon lafiya a kasar Sin sun sanar da killace wasu ma´aikatan gidan gona 15 don gudanar da nazari a kansu.

Hakan kuwa ya biyo bayan rasuwar tsuntsaye ne dubu goma sha biyar wanda keda nasaba da cutar murar tsuntsaye.

A cewar kamfaninin dillancin labaru na kasar, wato Xinhua bullar wannan cuta mai nau´in H5N1 a kasar ya zuwa yanzu ya haifar da kisan tsuntsaye na gida a kalla kusan dubu dari biyu.