1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kasashen Koriya za su kulla kawance da Amirka

Zulaiha Abubakar
March 6, 2018

Shugaban kasar Koriya ta Arewa Kim Jong Un ya goyi bayan batun babban taron Arewa da Kudu yayin da yake ganawa da wakilan shugaban kasar Koriya ta Kudu.

https://p.dw.com/p/2tkSq

Kafar yada labaran kasar ta sanar da cewar shugaba Jong Un, ya bayyana anniyar sa ta  bude sabon shafin tarihin hadin kan kasashen yayin liyafar cin abincin dare a jiya Litinin. Kasashen biyu da a baya dangantaka ta yi tsami a tsakanin su, sun daidaita ne dab da fara kakar wasanin bazara na Olymphics da aka kammala a Koriya ta Kudu,

Wakilai biyar daga cikin tawagar Koriya ta Kudu wadanda su ka hada da babban mai baiwa shugaban kasar shawara akan tsaro kuma jagoran tawagar Chung Eui Yong, sun gana da kusoshin gwamnatin Koriya ta Arewa a jiya Litinin don fara shirye shiryen inganta alakar kasashen biyu da kasar Amirka. Wannan dai shi ne karo na farko da Kim Jong Un, ya gana da manyan jami'an gwamnatin Koriya ta Kudu tun shekara ta 2011 da ya hau mulki.