1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kenya ta gaza daukar wasannin 'yan Afirka

Yusuf Bala Nayaya
September 24, 2017

An yanke wannan hukunci ne a wani zama da manyan jami'ai na hukumar CAF suka yi a birnin Accra na Ghana a ranar Asabar.

https://p.dw.com/p/2kbAv
Werbeball für den Afrika-Cup 2010
Hoto: picture-alliance/dpa/B. Fonseca

Kasar Kenya ta rasa dama ta daukar nauyin wasannin zakarun da ke taka kwallo a nahiyar Afirka ta CHAN a shekarar 2018 mai zuwa. Hukumar da ke tsara wasannin na Afirka CAF ta ce kasar ta Kenya ta yi nauyin jiki a kokari na shirye-shiryen karbar bakuncin wasannin na nahiyar da zakaru daga kasashe ke halarta.

An yanke wannan hukunci ne a wani zama da manyan jami'ai na hukumar suka yi a birnin Accra na Ghana a ranar Asabar kana a wannan rana ta Lahadi a ka bude dama ga sauran kasashen da ke da sha'awar daukar nauyin wasannin na CAF da su gwada ta su sa'ar su nema, kuma a cewar hukumar  kasashen da ke da muradi na da nan zuwa Lahadi mai zuwa su aika da bukatarsu, yayin da kasar da ta yi nasara za a bayyanata nan da makonni biyu.

An dai tsara buga wasannin ne tsakanin 12 ga watan Janairu zuwa hudu ga watan Fabirairu mai zuwa. Kamar Kenya ita Kamaru za a yi nazari kan shirye-shiryenta na karbar bakuncin wasannin a shekarar 2019.