Kotu ta amince da jinkirta zaben Kwango
October 18, 2016Talla
Kotun tsarin mulkin kasar Jamhuriyar Demokaradiyyar Kwango ta amince da bukatar hukumar zaben kasar kan jinkirta zabe. Ita dai hukumar zaben ta tsaya kai da fata tana bukutar lokaci domin sabunta sunayen masu zabe.
Wannan matakin ya nuna cewa ba za a gudanar da zabukan shugaban kasa, da 'yan majalisa, gami da yankuna ba har sai zuwa watan Afrilu na shekara ta 2018. Bisa tsarin mulki wa'adin Shugaba Joseph Kabila yana kawo karshe a watan Disamba mai zuwa.