1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu ta dakatar da sakin aure a Falasdinu

Salissou Boukari
May 28, 2017

Shugaban kotunan Musulunci na yankin Falasdinu Mahmoud Al-Habash, ya yi kira ga alkallan kotuna daban-daban da su dakatar da ayyana sakin aure a cikin wannan wata mai albarka na azumin Ramadana.

https://p.dw.com/p/2dhxJ
Palästina Gaza City Besuch Ai Weiwei
Mata a yankin Gaza na FalesdinuHoto: Getty Images/AFP/M. Abed

Cikin wata sanarwa da ya fitar, shugaban alkallan na Falasdinu ya ce ya dauki wannan mataki ne ta sabili da abubuwan da suka gani a shekarar da ta gabata, inda mutane suka yi ta sakin matayensu sannan daga bisani suka yi nadama.

A cikin wannan wata dai na Azumin Ramadan, wasu mutanen da ba su da abinci, ko kuma ba su samu sigarin da suka zuka ba, kan tayar da rikici a gidajensu, inda wani lokacin sukan daukan mataki na gaggawa na saki.