1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotu ta daure masu fyade a Chadi

Abdourahamane HassaneJuly 1, 2016

Wata kotu a kasar Chadi ta yanke hukuncin daurin shekaru goma tare da yin aikin badala ga wasu samarin guda shidda wadanda suka yi wa wata yar makarantar watau Zouhoura fyade.

https://p.dw.com/p/1JHld
Tschad Präsident Idriss Deby
Hoto: Reuters/T. Negeri

Shida daga cikin matasan guda takwas wadanda suka aikata fyaden akasarinsu suna da shekaru 16 zuwa 22 kuma suna daga cikin ya'yan manyan jami'an gwamnati.Uku daga cikin yara ya'yan wasu mayan sojoji ne na kasar ta Chadi masu mukamin Janar da kuma wani dan ministan harkokin waje.

Zouhoura 'yar shekau 17 samarin guda takwas sun yi mata fyade a cikin watan Maris da ya gabata.Biyu daga cikin matasa an yanke musu hukunci ba a kan idanusu ba domin kuwa sun arce zuwa kasashen waje: