1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kotun sauraron ƙarar maguɗin zaɓe ta soke zaɓen gwamnan jihar Kebbi

October 20, 2007
https://p.dw.com/p/Bu88
Kotun sauraron kararrakin magudin zabe a jihar Kebbi ta tarayyar Nijeriya ta yanke hukuncin cewa gwamnan Saidu Usman Dakin Gari yanzu ba shi ne gwamnan jihar ba dole sai an sake zabe. Mai shari´a Andrew Kaka shi ne ya yanke wannan hukunci bayan ya kafa hujjoji wadanda suka hada da cewar a lokacin da aka gudanar da zabe, gwamna Saidu Usman Dakin Gari ba cikakken dan jam´iyar PDP ba ne kuma a lokacin da ya canza sheka daga ANPP zuwa PDP babu cikakkun takardun da ke tabbatar da cewa ya bar jam´iyar ta ANPP. Kotun ta ba shi damar daukaka kara na wannan hukunci da ta yanke a yau.