1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar EU na dab da cimma matsaya da Kasashen Afrika

Kamaluddeen SaniNovember 12, 2015

Kungiyar EU sa ran cimma wata matsaya da shugabanin kasashen Afrika kan irin tallafin da EU za ta bayar don magance kwararar 'yan gudun hijirar Afrika zuwa Turai.

https://p.dw.com/p/1H4KT
Ägypten EU Afrika Treffen in Kairo Außenminister Ahmed Abul Gheit
Hoto: AP

Shugabanin kungiyar Tarayar Turai na shirye-shiryen kaiwa ga cimma wata matsaya akan wasu kudirori biyar da takwarorinsu daga nahiyar Afrika wajen bayar da tallafin kudade don kawar da matsalolin da ke janyo matsalar 'yan gudun hijira zuwa Turai.

Dukkanin bangarorin biyu na fatan ganin ta samu tagomashin kasashen tare da yin aiki tukuru a tsakaninsu wajen dakile safarar mutane da bazuwar 'yan gudun hijira gami da fadada tallafin taimako ga kasashen da matsalar tafi kamari.