1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar Hamas ta janye rundunar ta daga Zirin Gaza

May 26, 2006
https://p.dw.com/p/Buwh

Kungiyar Hamas dake jan ragamar hukumar mulkin cin gashin kan Falasdinawa ta janye sabuwar rundunar ´yan sanda da ta girke a Zirin Gaza a makon da ya gabata. Hamas ta ce ta dauki wannan mataki ne don hana barkewar sabon fada tsakanin ´yan sandan ta da na magoya bayan kungiyar Fatah ta shugaban Falasdinawa Mahmud Abbas.Wannan matakin ya zo ne a rana ta biyu a tarukan da ake yi da nufin yin sulhu tsakanin Hamas da Fatah, inda aka fi mayar da hankali akan batutuwan tsaro. Ko da ya ke Hamas ta lashe zaben ´yan majalisar dokoki da aka gudanar a cikin watan janeru, amma shugaba Mahmud Abbas ke iko da dakarun tsaro. Fadan na makon jiya a Zirin na Gaza yayi sanadiyar mutuwar akalla mutane 10.