1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar Hamas tace zata kalubalanci kuriar raba gardama

June 11, 2006
https://p.dw.com/p/BuuR

Kungiyar Hamas dake mulkin yankin Palasdinawa tace ta shirya kalubalantar shugaba Mahmud Abbas a gaban majalisa gobe litinin idan Allah ya kai mu,dangane da kuriar raba gardama da ya kira a gudanar,kan manhajar kasancewar kasar Palasdinu da Israila kafada da kafada.

Mahukuntan Hamas sunce majalisar dokokin zata gudanar da taron gaggawa gobe litinin,inda zasu mika shawarar gudanar da kuria a majalisar ta amincewa da kuriar ta raba gardama.

Kungiyar Hamas itake da rinjaye a majalisar mai bi mata kuma sai kungiyar Fatah ta shugaba Abbas wadda ta sha kaye a zaben watan janairu.

Shugaba Abbas dai yace yana da ikon kiran kuriar raba gardamar karkashin dokokin yankin Palasdinu.