1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

NATO za ta kara kaimi a Afghanistan

Abdourahamane HassaneJuly 9, 2016

Kungiyar tsaro ta NATO ta yanke shawarar bada karin tallafi ga kasar Afghanistan sakamakon halin da take ciki na tabarbarewar al'amuran tsaro.

https://p.dw.com/p/1JMIB
Polen Nato-Gipfel in Warschau - Angela Merkel & Tayyip Erdogan
Hoto: Reuters/K. Pempel

Shugabannin kasashe guda 28 na kungiyar tsaro ta NATO da ke yin taro a birnin Warsaw na kasar Poland a kwanaki na biyu jere sun tattara kudade kusan biliyan daya na dala, domin taimaka wa Amirka a cikin shekaru uku masu zuwa a game da shirinta na tsara rundunar sojojin Afghanistan. Jens Stoltenberg shi ne babban sakataren kungiyar tsaron ta NATO da ya yi karin haske.

Ya ce: ''Da farko mun amince mu cigaba da kawo wa rundanar kawance ta dakarun da ke a Afghanistan dauki har bayan wannan shekara da muke ciki har zuwa shekara ta 2020.''

A badi dai ana sa ran dakarun kasashen kawance hade da Amirka a Afghanistan din za su kai har dubu goma sha biyu.