1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar NLC ta janye yajin aki a Najeriya

Mouhamadou Awal BalarabeMay 22, 2016

A wani taro na majalisar koli da ta gudanar a Abuja ne Kungiyar NLC ta yanke hukuncin janye yajin aikin da ya biyo bayan janye tallafin man fetur.

https://p.dw.com/p/1IseW
1. Mai-Kundgebung in Abuja
Hoto: DW/Uwais Abubakar Idris

Daga cikin dalilan da ya kai NLC ga daukar wannan mataki, har da ganawa da daya daga cikin kusoshin jam'iyyar APC da ke mulki Bola Tinubu, wanda ya ba ta tabbacin tattaunawa da gwamnatin Najeriya kan janye tallafin man fetur.

Amma kungiyar kwadagon ta ce za ta ci gaba da tattauna ne kan matsayinta na cewa mai ya koma kan Naira 86 da Kobo 40 kowane lita, maimakon Naira 145. Amma za ta tattauna ne ba tare da yajin aiki ba.

Babu wani alkawari da NLC ta samu daga gwamnatin Buhari kan yanje tallafin man fetur. Sai dai wannan yajin aiki bai samu karbuwa ba a Najeriya.