1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar SADC ta cika shekaru 25

Abdourahamane Hassane
August 18, 2017

Kungiyar kasashen gabashin Afrika SADC na cika shekaru 25, yayin da ta ke taronta a Afrika ta Kudu. Ko ya zuwa yanzu kungiyar ta cimma a fannin maganta rigingimun siyasa da kuma na tattalin arziki?

https://p.dw.com/p/2iSZH
Ägypten Afrika-Treffen COMESA, EAC und SADC
Taron jagabannin kungiyar SADCHoto: Imago/Xinhua

Kasar Afrika ta Kudu na shirin karbar ragamar shugabancin kugiyar bunkasa tattalin arziki ta kasashen gabashin Afirka SADC a taron kungiyar da za a yi a birnin Pretoriya a ranar Asabar 19 ga wannan wata na Agusta, wanda shugaba Jacob Zuma zai karbi  jagorancin kungiyar daga Sarki Mswati na Swaziland. Ana sa ran shugaban na Afirka ta Kudu ya taka muhimiyar rawa a cikin kungiyar mai manbobi 15. Matsayin Afrika ta Kudu a cikin kungiyar, na da matsaloli, sakamakon yadda kasar ke daukar kanta a matsayin babbar yaya wadda kuma ke yin kaffa-kaffa wajen shiga cikin harkokin kasashen kungiyar wacce kuma ba ta shiga cikin kungiyar cinakayyar da ba mara shinge ba wada ta hada kasashen Swaziland da Bostwana da Lesotho da kuma kasar Namibiya.

 

Manufofin kungiyar bayan samar da ita.
Manufofin kungiyar wacce aka kafa ta 1992 a birnin Windoek na kasar Namibiya, su ne samar da zaman lafiya da jagoranci na kwarai a tsakanin kasahen da kuma huldar tattain arziki. A shekara ta 2008 kungiyar ta SADC ta cimma wata yarjejeniya cinikayya mara shinge, sai dai wasu kasashen ba su shiga ba saboda sun kauracewa yarjejeniyar, abin da ya sa har yanzu ci gaban da aka samu a cikin wasu kasashen kalilan ne, a cewar masharhanta. A cewarsu karara ta ke, ba a tsamanin kungiyar SADC za ta kasance ginshiki a fannin huldar kasuwanci marasa shingen tsakanin kasahen yankin a cikin lokaci kankani. 

Ägypten Scharm El-Scheich COMESA EAC SADC Gipfel
Hoto: Getty Images/AFP/K.Desouki

A farkon shekarun 1980 da aka girka kungiyar mai kama a haka wacce daga baya aka canza wa sunan manyan manufofinta a lokacin su ne na yaki da wariyar laubnin fata a Afrika ta Kudu  ta fannin kasuwanci wanda Afrika ta Kudu ta yi wa kasahen yankin fnitikau kuma fafutukar da sukayi ta ita ce ta rashin yin dogaro da Afrika ta Kudu. Babu shakka kungiyar ta SADC ta sha faman ganin an nemi hanyoyin tattaunawa da samun sulhu a Zimbabuwe domin kawo sauyi amma ba tare da cimma nasara ba, sannan wani abin da za a iya cewa nasara ce, shi ne rawar da kungiyar ta taka wajen hana juyin mulki a kasar Lesotho a shekarar 2014. Sai kuma a kasar Madagaska, inda can ma kungiyar ta taka rawa wajen warware rikicin siyasar kasar a shekara ta 2009.