1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kurdawan Siriya sun aikata manyan laifukan yaki

Salissou BoukariOctober 13, 2015

Kungiyar Amnesty International ta zargi mayakan Kurdawa na kasar Siriya masu samun goyon bayan Amirka, da aikata manyan laifukan yaki a garuruwan da suka kwace.

https://p.dw.com/p/1Gn29
Hoto: picture-alliance/dpa, Getty Images

Kungiyar dai ta zargi Kurdawan na Siriya da cin zarafin wadanda ba kurdawa ba tare da kone musu gidaje kurmus. A cikin wani rahoto ne mai shafuka 38 kungiyar mai kula da kare hakin dan Adam ta Amnesty International, ta ce ta tattauna da mutane kusan 40 da dukanninsu suka fuskanci mumunar muzgunawa daga mayaka na Kurdawa a garuruwan Rakka da Hassaka, bisa zarginsu na cewa suna da alaka da 'yan kungiyar IS. A cewar Lama Fakih mai ba da shawara a kungiyar ta Amnesty International, hukumomin na Kurdawa ko kadan ba sa mutunta dokokin kasa da kasa kan hakkin dan Adam.