1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kuwaiti: Ana gudanar da zaben 'yan majalisa.

November 26, 2016

Al'ummar Kuwaiti na zaben 'yan majalisa, a wannan karamar kasa mai arzikin mai, wadda ke fama da matsalar tattali sakamakon faduwar darajar mai a kasuwannin duniya.

https://p.dw.com/p/2TIYc
Kuwait Parlamentswahlen 2016
Hoto: Getty Images/AFP/Y. Al-Zayyat

Zaben ya biyo bayan rusa majalisar dokokin kasar da Sarki ya yi a watan Oktoban da ya gabata, biyo bayan rage kudaden gudanar da karin farashin makamashin gas.

 

Kuwaiti ta kasance kasa daya tilo tsakanin takwarorinta masu arziki na yankin Gulf, da ke da tsarin siyasa mai sassauci, duk da cewar Basaraken kasar ne keda wuka da nama akan komai.

 

Majalisar mai wakilai 50 na da hurumin binciken ministoci, ciki har da wadanda suka fito daga gidan sarauta. Sai dai a baya-bayan nan afkawa 'yan adawa da kame kamesu, da sauya dokokin zabe, na dasa ayar tambaya dangane da ko sakamakon zaben na yau zai iya haifar da wani sauyi.