1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwalambiya: 'Yan tawayen ELN sun sako dan majalisa

Gazali Abdou Tasawa
February 2, 2017

Kungiyar 'yan tawayen ELN a Kwalambiya ta sanar da sako a wannan Alhamis tsohon dan majalisar nan na kasar Odin Sanchez wanda take garkuwa da shi yau kusan watanni goma.

https://p.dw.com/p/2Wt0C
Kolumbien ELN Rebellen
Hoto: Getty Images/AFP/P. Ugarte

Sakin tsohon dan majalisar Odin Sanchez mai shekaru 61 na daga cikin sharuddan da dama gwamnatin Kwalambiyar ta gindaya wa kungiyar tawayen kafin soma duk wata tattaunawa. Sai dai a cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Twitter Kungiyar tawayen ta ELN ta ce a yanzu ya rage ga gwamnatin kasar ta Kwalambiya da ta cika alkawarin da ta dauka na yin afuwa ga wasu kumandojinta biyu da ake tsare da su a gidan wakafi. 

Kungiyar tawayen ta ELN ta ce Odin Sanchez na yanzu haka a hannun kwamitin kiyon lafiya na kungiyar, kuma nan gaba kadan za a dauke shi ta jirgi mai dirar ungulu zuwa birnin Choco na arewa maso gabashin kasar domin mika shi ga hannun hukumomi.