1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kwamitin Sulhu ya yi tir da furucin shugaba Ahmedi Nejad na kyamar Isra´ila

December 10, 2005
https://p.dw.com/p/BvHB

Kwamitin sulhu na MDD ya shiga sahun kasashen duniya wajen yin tir da furucin da shugaban Iran Mahmud Ahmedinejad yayi na nuna kyamar Isra´ila. A cikin wani kuduri da ya zartas kwamitin sulhu ya ce haramun ne wata membar kwamitin ta yi barazana ga ´yanci da wanzuwar wata kasa. A ranar alhamis da ta gabata shugaba Ahmedinejad ya kwatanta Isra´ila da wata cutar cancer sannan ya ce kamata yayi a mayar da kasar ta bani Yahudu a wani yanki dake tsakanin Jamus da Austria. Hakazalika shugaban ya yi suka da yadda ake ba da muhimmanci ga kisan kare dangi da gwamnatin Nazi ta yiwa Yahudawa a lokacin yakin duniya na biyu. A halin da ake ciki ma´aikatun harkokin wajen biranen Berlin da Vienna sun ba da takardun sammaci ga jakadun Iran dake kasashen su don nuna adawa da furucin na shugaba Ahmedinejad.