1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Libiya: Karbe iko da cibiyoyin fidda mai

Ahmed SalisuSeptember 11, 2016

Sojojin da ke biyayya ga Janar din na Libiya wati Khalifa Haftar sun bayyana cewar sun karbe iko da tashoshin jiragen ruwa da ake fidda danyen mai a kasar.

https://p.dw.com/p/1K073
Verteilerkreuz einer Ölleitung der Firma Wintershall
Hoto: picture-alliance/dpa

Masu aiko da rahotanni suka ce an tafaka kazamin fada kafin kaiwa ga karbe iko da tashoshin kamar yadda bangaren Janar Haftar din ya tabbatar, lamarin da ya sanya manzo musamman na MDD da a kasar Martin Kobler nuna damuwarsa game da wannan rikici. Wannan dai ba karamin koma baya baya ne ga gwamnatin kasar da ke Tripoli, wadda ke samun goyon bayan kasashen duniya duba da cewar babbar hanyar samun kudin shigarta ya koma ga hannun wanda ke adawa da ita.